Al’ummar garin Ganduje sun nuna rashin amincewa da cire Dagacinsu-Sulaiman Ganduje.

Al’ummar Garin Ganduje sun nuna rashin amincewarsu da sauke Dagacin Ganduje a yankin Karamar Hukumar Dawakin Tofa.

Inda suna kaiwa Sarkin Kano 15, Aminu Ado Bayero gaisuwar Bangirma bisa jagorancin Dr Hussaini Umar Ganduje.

Guda cikin Yan Tawagar al’ummar Ganduje, Suleiman Isma’il Ganduje, yace sun samu rakiyar Dr. Hussain Umar Ganduje, inda suka shedawa Sarki na 15, Alh. Aminu Ado Bayero halin da suke ciki, tare da nuna mubaya’arsu gareshi.

Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started