Matashin da ya kwaci wayar wata mata mota ta kadeshi ya rasu

Daga Abubakar Sale Yakub

Mai kwacen wayan nan da mota ta buge shi a Kano ya rigamu gidan gaskiya , a cewar rundunar ’yan sandan jihar Kano.

A safiyar ranar Talata ce mai kwacen wayan ya ce ga garinku nan a inda aka kwantar da shi,  a Asibitin Murtala,  inji kakakin rundunar, Abdullahi Harun Kiyawa, ya sanar.

GASKIYATA ta ruwaito cewa a ranar Lahadi mota ta buge mai kwacen wayar lokacin da yake kokarin tserewa bayan ya yi wa wata mata fashin wayarta a Titin gidan zoo.

Kakakin ’yan sandan jihar Kano, Haruna Abdullahi Kiyawa, ya ce mota ta kade shi ne a yayin da yake kokarin tsallaka titi bayan ya yi fashin.





Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started