Karancin Naira ya yi kamari a Abuja yayin da na’urar ATM ta kasa rarraba kudi
Wasu sassa na babban birnin tarayya, FCT, sun fara fuskantar karancin kudin Naira, a daidai lokacin da ‘yan Najeriya ke fara bukukuwan Kirsimeti.
A kalla bankunan kasuwanci guda bakwai a unguwar AYA da ke Abuja sun kasa raba kudi a ranar Alhamis.
Wakilin DAILY POST, wanda ya ziyarci wadannan na’urorin ATM a yammacin ranar Alhamis, ya ruwaito cewa bai iya janyewa ba, kuma kusan mako guda kenan lamarin.
Wakilinmu, ya lura cewa, masu POS, sun yi layi a bankunan domin samun kudade dan gudanar da sana’ar su .
Daya daga cikin masu sana’ar POS, wanda ya bayyana kansa a matsayin Samuel, ya koka da yadda na’urorin ATM din ba sa raba kudi kamar yadda ake tsammani.
“Tun da muka shiga watan Disamba wadannan na’urorin ATM din basa bayar da kudi so sai.
“Akwai karanci naira kuma mai yiyuwa ne saboda muna cikin watan Disamba, amma CBN ne kadai zai iya bayyana wannan sabon karancin,” inji shi.
Wannan na zuwa ne a daidai lokacin da Babban Bankin Najeriya CBN ya ba da umarnin cewa duka tsofaffin takardun Naira za a cigaba da amfani dasu bisa doka a Najeriya.
Kotun koli a hukuncin da ta yanke ta amince da bukatar gwamnatin tarayya ta neman ta dage wa’adin ranar 31 ga watan Disamba kan amfani da kudi N200, N500, da N1,000.
Yayin da yake mayar da martani kan hukuncin, CBN ya ce: “Don kauce wa shakku, Kotun Koli ta ba da umarnin cewa tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1000, tare da sake fasalin su, za su ci gaba da zama doka.
“Saboda haka, bisa ga sashe na 20 (5) na dokar CBN ta shekarar 2007, duk takardun kudi da babban bankin Najeriya ya fitar za su ci gaba da zama a kan doka har abada.”
Leave a comment