Limaman Masallatan Juma’a na Kano  ku daina yin huduba kan abin da baku da iliminsa.. Sheik Muhd Nasir Adam

Sheik Muhammad Nasir Adam

Shugaban Majalisar limaman Juma’a na jahar Kano Sheik MUHAMMAD Nasir Adam ya nemi Limamai su yi addu’o’i a ranar Juma’a me zuwa don samun zaman lafiya a lokutan  gudanar campaign da zabuka dake tafe.

Ya yi kiranne a lokacin da ya ke zantawa da wakilin mu Abubakar Sale Yakub, a birnin Kano ya  bukaci ‘Yan siyasa  dasu kaucewa yin amfani da matasa domin haifar da rikici, Shehin Malamin ya ja hankalin iyaye dasu lura da Kai komon ya yansu.

Sheik Muhammad Nasir Adam, ya cigaba  da yin kira ga Limaman Jihar Kano, dasu kaucewa yin huduba   akan duk kan wani lamari  da basu da hakikanin iliminsa.
ASY

Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started